Gwamnan Kano ya Turawa Majalisar Dokoki Sunayen Kantomomi 44 Domin Tantancewa

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gwamna Abba Kabir-Yusuf na jihar Kano ya mika sunayen shugabannin riko na kananan hukumomin jihar ga majalisar dokokin jihar ta domin tantance su.

Wannan na zuwa ne makonni uku, bayan karewar wa’adin zababbun shugabannin kananan hukumomin jihar.

Kakakin majalisar, Ismail Falgore, ne ya bayyana hakan a ranar Talata a zauren majalisar yayin da yake karanta takardar bukatar da gwamnan ya turawa majalisar.

Gwamna Abba Kabir Ya Mikawa Majalisar Kano Sunayen Kwamishinonin Da Zai Nada

Yayin da yake gabatar da sakon, shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini (NNPP-Dala), ya ce bukatar gwamnan ta biyo bayan karewar wa’adin zababbun shugabannin kananan hukumomin da mataimakansu ne tun a ranar 12 ga watan Fabrairu, 2023.

A cewarsa, jerin sunayen sun kunshi shugaba da mataimakinsa da sakatare na kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomi 44 da ake da su a jihar.

Bidiyon Dala: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Karar da Ganduje Ya Kai Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano

Shugaban masu rinjaye ya bayyana cewa sashe na 58 na dokar kananan hukumomi ya bayyana cewa, idan wa’adin shugabancin kananan hukumomin jihar ya kare ya zama wajibi a gudanar da zabe.

Dokar ta kuma bayyana cewa gwamna na iya nada shuwagabannin riko da za su rika kula da harkokin majalisun kananan hukumomin na tsawon watanni uku.

Bayan tattaunawa, majalisar ta amince da kudurin, tare da kafa kwamitin wucin gadi da zai tantance wadanda aka nada a ranar Laraba 6 ga watan Maris.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...