Kamata yayi Gwamnati ta cirewa kayan masarufi haraji ta mai dashi kan Giya, sigari da kayan kyalekyale – Falakin Shinkafi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Falakin Shinkafi Ambassador (Dr) Yunusa Yusuf Hamza, ya shawarci gwamnatin tarayyar Nigeria da ta bada umarni ga hukumar hana fasa kwauri ta kasa (Costum) rika sassautawa yan Kasuwa musamman ta fuskar biyan harajin kayan masarufi domin fitar da yan kasar daga mawuyacin halin da suke ciki.

” Babu shakka matakan da gwamnati ta fara dauka na magance matsalar hauhawar farashin Dala musamman barazanar daukar mataki akan harkar Kirifto, amma bayan wannan akwai wasu matakai da muke ganin idan an dauke su zasu taimaka wajen magance matsalar mawuyacin halin da al’umma suke ciki”.

Falakin Shinkafi ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da Jaridar kadaura24 a Kano.

” Mafi yawan yan kasuwar Suna Kokawa da yadda jami’an Kwastam suke tsauwala musu ta fuskanta karbar kuɗin haraji da lissafin Dala, sannan kuma bai dace a rika yin irin tsarin ma, kamata yayi a rika amfani da kuɗin mu na Naira tunda dai so ake a saukakawa al’umma”. Inji Falakin Shinkafi

Kotun ta Yanke Hukunci Kan Kalubalantar Hukuncin Kashe Sheikh Abduljabbar

Amb. Yunusa Yusuf wanda kuma shi ne Jarman Matasan Arewa, ya ce matukar gwamnatin Najeriya tana bukatar al’umma su sami sauki dole ne sai ta sassautawa yan kasuwa ta hanyar karbar kudaden harajin kayan masarufi, wanda idan an tsauwala musu wajen kiliyarans to su ma zasu sassautawa al’umma masu siyan kayansu, haka ma idan aka tsauwala musu suma sai sun tsauwalawa al’umma masu siyan kayansu.

” Haka kuma akwai bukatar gwamnatin tarayyar tafi mai da hankali wajen karbar haraji ga kayan da basu da muhimmaci kamar sigari giya da sauran kayan kyalekyale, maimakon kayan masarufi wadanda sune al’umma suka fi bukatarsu a yau da kullum”. A cewar Falakin Shinkafi

Majalisar dokokin jihar Kano ta bankado badakalar kudi a wasu hukumomin gwamnati

Game da batun cire tallafin wutar lantarki da gwamnati ta ce zata yi, Amb. Yunusa Yusuf Hamza yace bai kamata gwamnatin ta cire tallafin ba a irin wannan lokaci da al’umma suke cikin radadin cire tallafin man fetur.

” Ko shakka babu idan aka cire tallafin wutar al’umma zasu kara shiga cikin mawuyacin hali, don haka muna shawartar shugaban kasa da duk masu ruwa da tsaki a harkar da su tabbatar ba’a cire tallafin wutar lantarki a Nigeria ba”. Inji Falakin Shinkafi

Yace waɗannan abubunwan da ya fada idan gwamnatin tarayyar Nigeria ta karbe su kuma ta aiwatar da su, babu shakka al’ummar kasar zasu sami saukin na mawuyacin halin tsadar rayuwar da suke ciki a yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...