Yadda Matasa a Kano suka gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Matasa maza da mata da dama a jihar Kano sun sufi domin gudanar da zanga-zanga, don nuna adawarsa da tsadar kayan masarufi da ake fuskanta a Nigeria .

Masu Zanga-zangar dai sun fito ɗauke da kwalaye, inda suke rera waƙa mai taken “Tsadar Rayuwa ba zamu iya ba”, a ƙoƙarin da suke yi na nunawa da nu halin da suke ciki.

Matasan waɗanda suka futo fuskokinsu a murtuke, sun gudanar da zanga-zangar ne yau Alhamis a unguwannin Bachirwa, Kurna da kuma Rijiyar lemo, dake kan titin zuwa katsina a Kano.

Da dumi-dumi: Kungiyar Kwadago ta Bayyana Ranar Fara Yajin Aiki a Nigeria

Haka kuma Masu Zanga-zangar dai sun ce Rayuwar tayi musu matuƙar wahala, a sakamakon yadda abinci yake neman gagararsu, balle aje ga sauran Buƙatu na Rayuwa.

Baya ga haka sunce kayan masarufi yana neman gagararsu, saboda yadda abubuwa da yawa suka ninka kuɗin su sama da sau biyar, wasu mah Sai goma.

Jinkirin biyan albashi: Ma’aikatan gwamnati sun kalubalanci Tinubu

Adan haka suka fito zanga-zangar, dan nuna fushin su da salon kamun ludayin Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, duba da yadda yake neman kassara Rayuwarsu.

A ƙarshe sunyi fatan dukkan masu ruwa da tsaki zasu yi dukkan abubuwan da suka kamata, domin kawo wa Talakawan Najeriya ɗauki daga wannan hali da suke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...