Da dumi-dumi: Kungiyar Kwadago ta Bayyana Ranar Fara Yajin Aiki a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Kungiyoyin kwadago a Najeriya NLC da TUC sun baiwa gwamnatin tarayya wa’adin Kwanaki 14 ta cika alkawurin da suka kulla ko su tsunduma yajin aiki a fadin Kasar.

Koken nasu ya samo asali ne daga rashin aiwatar da yarjejeniya 16 da aka kulla tsakanin kungiyoyin kwadago (NLC da TUC) da gwamnatin tarayya a ranar 2 ga Oktoba, 2023.

Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano ta Bayyana Yadda Zata Yaki Yan Kasuwa Masu Boye Kayan Masarufi

Shugabannin kungiyoyin NLC da TUC sun bayyana damuwarsu da cewa, duk da kokarin da kungiyoyin kwadago ke yi na inganta zaman lafiya a ma’aikatu, ga dukkan alamu gwamnati ba ta damu da wahalhalun da al’umma suke ciki ba .

Tsadar Kayan Abinchi: Kotu Ta Baiwa Gwamnatin tarayya Umarni

NLC da TUC, a cikin wata sanarwa da suka fitar, sun koka da cewa “abin takaici ne yadda aka tilasta mana daukar irin wadancan matakan, amma rashin kula da walwalar ‘yan kasa da ma’aikatan Najeriya da kuma tsananin wahala ya sa ba mu da zabi sai mun yi haka.”

“Sakamakon wannan ci gaba tare da sanin muhimmancin tabbatar da tsaro da kare hakki da mutuncin ma’aikatan Najeriya da ‘yan kasa, kungiyar NLC da TUC sun ba da wa’adi ga gwamnatin tarayya da ta mutunta yarjejeniya cikin kwanaki 14 daga gobe, ranar 9 ga Fabrairu 2024.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...