Sojoji sun Kubutar da Sojan da Yan Bindiga Su ka Sace a NDA

Date:

Sojoji sun ceto Manjo CL Datong, wanda yan bindiga suka sace daga Makarantar Tsaro ta Najeriya (NDA) kwanaki 21 bayan faruwar lamarin.

An yi garkuwa da babban jami’in ne bayan da ‘yan bindiga suka kutsa kai cikin hukumar NDA inda suka kashe jami’ai biyu.

Da yake ba bayyana yadda aka kubutar da shi, rundunar sojin Najeriya a cikin wata sanarwa Mai dauke da sa hannun mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar ta 1 ta sojojin Najeriya, Kanal Ezindu Idimah, ya ce rundunar sojojin Najeriya tare da rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) da dukkan hukumomin tsaro sun sun gudanar da wani gagarumin aiki hadin don kubutar da Manjo.

Ya bayyana cewa bayan rusa sansanin ‘yan ta’adda da dama da aka gano a yankin Afaka- Birnin Gwari tare da kashe’ yan ta’adda da yawa, sojoji sun isa sansanin da ake zargi shine wurin da ake tsare da Maj CL Datong

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...