Da dumi-dumi: Buhari ya Sauke Sanata Lado daga Shugabancin NAPTIP

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauke Sanata Basheer Mohammed Lado Daga kujerar Darakta Janar na hukumar hana fataucin mutane ta kasa (NAPTIP).

An sauke Mohammed Lado ne kasa da watanni hudu bayan ya karbi ragamar hukumar.

A cikin wata sanarwa a ranar Laraba, Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Kafafen Yada Labarai, Garba Shehu, ya ce shugaban ya amince da nadin Fatima Waziri-Azi a matsayin wanda zata maye gurbin Sanata Lado.

Garba Shehu ya ce nadin ya biyo bayan shawarar da ministar kula da ayyukan jin kai da kula da bala’i da ci gaban al’umma Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Kadaura24 ta rawaito an musanyawa Mohammed Lado mukaminsa na Babban Kwamishinan a Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira zuwa Hukumar Naptip Kasa da watanni 4 da Suka gabata.

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...