Da dumi-dumi: Buhari ya Sauke Sanata Lado daga Shugabancin NAPTIP

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauke Sanata Basheer Mohammed Lado Daga kujerar Darakta Janar na hukumar hana fataucin mutane ta kasa (NAPTIP).

An sauke Mohammed Lado ne kasa da watanni hudu bayan ya karbi ragamar hukumar.

A cikin wata sanarwa a ranar Laraba, Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Kafafen Yada Labarai, Garba Shehu, ya ce shugaban ya amince da nadin Fatima Waziri-Azi a matsayin wanda zata maye gurbin Sanata Lado.

Garba Shehu ya ce nadin ya biyo bayan shawarar da ministar kula da ayyukan jin kai da kula da bala’i da ci gaban al’umma Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Kadaura24 ta rawaito an musanyawa Mohammed Lado mukaminsa na Babban Kwamishinan a Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira zuwa Hukumar Naptip Kasa da watanni 4 da Suka gabata.

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...