Yanzu-Yanzu: EFCC ta tsare Bukola Saraki

Date:

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta’annati, EFCC , ta ce ta tsare tsohon shugaban majalisar dattawan kasar, Sanata Bukola Saraki.

Mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren, ya tabbatar wa BBC cewa sun gayyaci Sanata Saraki ne domin ya amsa wasu tambayoyi game da zarge-zargen cin hanci.

Sai dai bai yi cikakken bayani kan zarge-zargen da suke yi wa tsohon gwamnan jihar ta Kwara ba.

Amma kafofin watsa labaran kasar sun bayyana cewa ana tuhumar Sanata Saraki ne bisa zarge-zargen sata da halasta kudin haramun.

Sanata Saraki, wanda ya shafe shekaru takwas a matsayin gwamnan jihar Kwara, ya daɗe yana fuskantar zargin cin hanci da kuma halatta kudin haramun.

A baya ya fuskanci shari’a bisa zargin kin bayyana kaddarorinsa amma Kotun Kolin Najeriya ta wanke shi a shekara ta 2018.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...