Zargin Rashawa: EFCC ta kama tsohon gwamnan Nasarawa Tanko Al-Makura da matarsa

Date:

Hukumar EFCC a Najeriya ta kama tsohon gwamnan Nasarawa kuma sanata a yanzu Umaru Tanko Al-Makura da matarsa kan rashawa.

Jaridar Premium Times a Najeriyar ta rawaito cewa yanzu haka ana riƙe da tsohon gwamnan da matarsa a ofishin EFCC da ke Abuja.

Jaridar ta ce duk da cewa babu wasu cikakkun bayanai, majiyoyi na tabbatar da cewa kamen na da alaƙa da rashawa da aka tafka a mulkin shekara 8 da ya yi na gwamna a Nasarawa.

Al-Makura ya jagoranci Nasarawa daga shekara ta 2011 zuwa 2019 kafin daga bisani ya tafi majalisa a matsayin Sanata mai wakiltar Nasarawa ta kudu.

68 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...