Zargin Rashawa: EFCC ta kama tsohon gwamnan Nasarawa Tanko Al-Makura da matarsa

Date:

Hukumar EFCC a Najeriya ta kama tsohon gwamnan Nasarawa kuma sanata a yanzu Umaru Tanko Al-Makura da matarsa kan rashawa.

Jaridar Premium Times a Najeriyar ta rawaito cewa yanzu haka ana riƙe da tsohon gwamnan da matarsa a ofishin EFCC da ke Abuja.

Jaridar ta ce duk da cewa babu wasu cikakkun bayanai, majiyoyi na tabbatar da cewa kamen na da alaƙa da rashawa da aka tafka a mulkin shekara 8 da ya yi na gwamna a Nasarawa.

Al-Makura ya jagoranci Nasarawa daga shekara ta 2011 zuwa 2019 kafin daga bisani ya tafi majalisa a matsayin Sanata mai wakiltar Nasarawa ta kudu.

68 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...