Ba za mu lamunci afkawa kayan al’umma da sunan ganima ba – Abba Gida-gida

Date:

Daga Maryam Ibrahim Muhammad

 

Gwamnatin Jihar Kano na sanar da al’ummar Jihar cewa ba za ta lamunci afka wa gine-ginen mutane da sunan cin ganima ba, a dukkan sassan jihar.

Hotuna: Wasu matasa sun farwa sabbin shagunan tsohuwar Triumph dake Fagge

Haka kuma gwamnati na bayyana takaicin ta bisa yadda wasu Matasa suka afka wa ginin dake cikin tsohon gidan jaridar Triump da ke Fagge alhalin wannan ginin baya cikin lissafin wuraren da za a rushe.

 

Wannan sanarwa ce da gargaɗi daga ofishin Sakataren Gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi.

Sabo da haka gwamnatin na ƙara jadadda cewar duk wanda aka samu da laifin afka wa wani gini tare da kwashe kayayyakin jikin sa zai gamu da fushin hukuma.

 

Gwamnatin ta ƙudiri aniyar yin aiki ne domin ci gaban Jihar Kano ba domin bai wa wasu lasisin rushe gine-gine da sace kayan mutane babu gaira babu dalili ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...