Daga Maryam Ibrahim Muhammad
Gwamnatin Jihar Kano na sanar da alβummar Jihar cewa ba za ta lamunci afka wa gine-ginen mutane da sunan cin ganima ba, a dukkan sassan jihar.
Hotuna: Wasu matasa sun farwa sabbin shagunan tsohuwar Triumph dake Fagge
Haka kuma gwamnati na bayyana takaicin ta bisa yadda wasu Matasa suka afka wa ginin dake cikin tsohon gidan jaridar Triump da ke Fagge alhalin wannan ginin baya cikin lissafin wuraren da za a rushe.
Wannan sanarwa ce da gargaΙi daga ofishin Sakataren Gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi.
Sabo da haka gwamnatin na Ζara jadadda cewar duk wanda aka samu da laifin afka wa wani gini tare da kwashe kayayyakin jikin sa zai gamu da fushin hukuma.
Gwamnatin ta Ζudiri aniyar yin aiki ne domin ci gaban Jihar Kano ba domin bai wa wasu lasisin rushe gine-gine da sace kayan mutane babu gaira babu dalili ba.