Wahalar Mai: Tinubu ya gana da Emefiele, Kyari a Villa

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Shugaban kasa Bola Tinubu zai fara aikinsa a matsayin shugaban Najeriya tare da ganawa da gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele, da shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari a fadar gwamnatin tarayya .

Duk da cewa ba a bayyana makasudin taron a hukumance ba, jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa taron ba zai rasa nasaba da rikicin da ake samu na cire tallafin man fetur wanda tun daga lokacin ya jefa ‘yan Najeriya cikin fargaba.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Tinubu ya shiga fadar shugaban kasa a ranar Talata, inda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da wasu manyan jami’an gwamnati suka tarbe shi a kofar ofishinsa.

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da kakakin majalisar Femi Gbajabiamila da babban sakataren fadar shugaban kasa Tijjani Umar, tsohon kwamishinan kudi na Legas, Wale Edun; Dele Alake; James Faleke.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...