Tsohon Firaministan Burtaniya ya ziyarci Tinubu a Abuja

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Zaɓaɓɓen Shugaban kasar Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya karbi bakuncin tsohon firaministan Birtaniya Tony Blair a babban birnin tarayya Abuja.

 

” Zamu haɗa kai da cibiyar koyar da ingantacciyar gwamnati ta Tony Blair domin samawa al’ummar Nigeria ingantacciyar rayuwa, a kokarin mu na samar da sauƙi ga al’ummar kasa Nigeria”. Inji Tinubu

 

Tinubu ne ya bayyana hakan a sashihin shafin sa na Facebook a yammacin wannan rana .

” Mun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da kuma yadda Najeriya za ta ci gaba da cin gajiyar ayyukan ban mamaki na Cibiyar don kyautata rayuwar al’umma”.

Ana ganin dai Bola Tinubu zai yada kai da cibiyoyi makamantan wannan domin inganta rayuwar al’ummar Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...