Doguwa ya janye daga takarar shugabancin majalisa, zai marawa wani baya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya janye kudirinsa na neman shugabancin majalisar wakilai ta 10, Inda ya bayyana goyon bayansa ga Tajudeen Abbas.

 

Doguwa ya jagoranci wasu ‘yan takara biyu Abubakar Makki da Tunji Oluwuyi, inda suka janye daga takararsu a ranar Larabar da ta gabata yayin wani taro da kungiyar hadin gwiwa ta shirya, kamar yadda rahoton Daily Post ya nuna.

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da wasu aiyuka – Ganduje

Idan dai ba a manta ba kadaura24 ta rawaito jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Abbas da Ben Kalu a matsayin shugaban majalisar da mataimakinsa, lamarin da ya haifar da cheche-ku ce a tsakanin ‘yan takarar.

A baya dai Doguwa ya bi sahun wasu masu kalubalantar Abbas, Amma kuma yanzu ya aminta zai marasa masa baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...