Doguwa ya janye daga takarar shugabancin majalisa, zai marawa wani baya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya janye kudirinsa na neman shugabancin majalisar wakilai ta 10, Inda ya bayyana goyon bayansa ga Tajudeen Abbas.

 

Doguwa ya jagoranci wasu ‘yan takara biyu Abubakar Makki da Tunji Oluwuyi, inda suka janye daga takararsu a ranar Larabar da ta gabata yayin wani taro da kungiyar hadin gwiwa ta shirya, kamar yadda rahoton Daily Post ya nuna.

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da wasu aiyuka – Ganduje

Idan dai ba a manta ba kadaura24 ta rawaito jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Abbas da Ben Kalu a matsayin shugaban majalisar da mataimakinsa, lamarin da ya haifar da cheche-ku ce a tsakanin ‘yan takarar.

A baya dai Doguwa ya bi sahun wasu masu kalubalantar Abbas, Amma kuma yanzu ya aminta zai marasa masa baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...