Yan Sanda sun kama kwamishinan Zaɓen Adamawa Hudu Ari

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Rundunar ‘yan sandan ta kasa ta ce ta kama kwamishinan zaɓen jihar Adamawa da aka dakatar.

 

Matakin da kwamishinan zaɓen na jihar Adamawa ya ɗauka a lokacin zaɓen 15 ga watan Afrilu ya janyo ruɗani, bayan ya bayyana Binani a matsayin wadda ta yi nasara duk da yake ba a kammala tattara sakamako ba.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce jami’an rundunar masu bibiyar harkokin zaɓe ne suka kama Hudu Ari, ranar Talata a Abuja babban birnin ƙasar.

Ba wani ma’aikaci a Kano da yake bina ko sisin kobo – Ganduje ya bugi Kirji

sanarwar ta ce kwamishinan na INEC yana hannunta don amsa tambayayoyi kan tuhume-tuhumen da ake masa game da ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara a zaɓen cike giɓi da aka gudanar ranar 15 ga watan Afrilu.

 

Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya ce rundunar za ta kama duk mutanen da ke da hannu a lamarin domin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanada.

Hajjin bana: Jirgin Max Air NAHCON ta baiwa aikin jigilar maniyyatan Kano – Abba Danbatta

Ya kuma sake jaddada ƙudurin ‘yan sandan wajen tabbatar da adalci a cikin lamarin tare da gurfanar da duk mutanen da ke da hannu a lamarin gaban kotu.

 

Lamarin ya sanya hukumar zaɓe ta INEC ta dakatar da Ari, yayin da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da umurnin gudanar da bincike a kan sa, da kuma jami’an tsaron da suka ba shi kariya a lokacin da abin ya faru.

 

A wata ganawa da manema labarai Hudu Ari ya musanta zargin da ake yi cewa ya karɓi cin hancin naira biliyan biyu, kafin ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...