Yan Sanda sun kama kwamishinan Zaɓen Adamawa Hudu Ari

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Rundunar ‘yan sandan ta kasa ta ce ta kama kwamishinan zaɓen jihar Adamawa da aka dakatar.

 

Matakin da kwamishinan zaɓen na jihar Adamawa ya ɗauka a lokacin zaɓen 15 ga watan Afrilu ya janyo ruɗani, bayan ya bayyana Binani a matsayin wadda ta yi nasara duk da yake ba a kammala tattara sakamako ba.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce jami’an rundunar masu bibiyar harkokin zaɓe ne suka kama Hudu Ari, ranar Talata a Abuja babban birnin ƙasar.

Ba wani ma’aikaci a Kano da yake bina ko sisin kobo – Ganduje ya bugi Kirji

sanarwar ta ce kwamishinan na INEC yana hannunta don amsa tambayayoyi kan tuhume-tuhumen da ake masa game da ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara a zaɓen cike giɓi da aka gudanar ranar 15 ga watan Afrilu.

 

Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya ce rundunar za ta kama duk mutanen da ke da hannu a lamarin domin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanada.

Hajjin bana: Jirgin Max Air NAHCON ta baiwa aikin jigilar maniyyatan Kano – Abba Danbatta

Ya kuma sake jaddada ƙudurin ‘yan sandan wajen tabbatar da adalci a cikin lamarin tare da gurfanar da duk mutanen da ke da hannu a lamarin gaban kotu.

 

Lamarin ya sanya hukumar zaɓe ta INEC ta dakatar da Ari, yayin da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da umurnin gudanar da bincike a kan sa, da kuma jami’an tsaron da suka ba shi kariya a lokacin da abin ya faru.

 

A wata ganawa da manema labarai Hudu Ari ya musanta zargin da ake yi cewa ya karɓi cin hancin naira biliyan biyu, kafin ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...