Yakin Sudan: Rukunin farkon na daliban Najeriya sun Isa Ƙasar Masar – Gwamnatin tarayya

Date:

 

Rukunin farko na daliban Najeriya da aka kwashe daga kasar Sudan sun isa kan iyakar Aswan na kasar Masar a ranar Alhamis 27 ga watan Afrilu.

Shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM) Abike Dabiri-Erewa ta bayyana hakan a shafinta na Twitter a daren Alhamis.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya halarci Faretin Sojoji Sanye da kakin Soji

Rukunin farkon sun isa kan iyakar Aswan ta ƙasar Masar, amma an riga an rufe iyakar a lokacin da suka Isa, amma a su tashi da sassafe sannan su wuce filin jirgin sama,” in ji abike

Yakin Sudan: An kaiwa daliban Nigeria hari

Hakazalika, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa ta ce rukunin farko na ‘yan Najeriya daga Sudan sun riga sun isa iyakar kasar Masar kuma za a kawo su Najeriya a yau Juma’a.

 

Mataimaki na musamman ga Darakta Janar na NEMA, Idris Muhammad, a ranar Juma’a ta gidan talabijin na Channels, Sunrise Daily, ya tabbatar da isowar rukunin farko na ‘yan Najeriya a kan iyakar ta Masar.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa wasu daga cikin daliban Najeriya sun kokan kan yadda aka bar su cikin mawuyacin hali a Sahara a jiya Alhamis.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...