Gwamnatin tarayya ta dakatar da cire tallafin man fetur

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Majalisar kula da tattalin arziƙin Najeriya ta ce ba yanzu ne lokacin da ya dace a cire tallafin man fetur ba a ƙasar.

 

Ministar Kuɗi da tsare-tsare ta ƙasa Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan bayan kammala taron Majalisar da aka yi a ranar Alhamis, wanda mataimakin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar gwamnati.

 

Ta ce za a ci gaba da dukkan ayyukan da aka fara game da shirin cire tallafin na tuntubar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki, ciki har da wakilan sabuwar gwamnati mai jiran gado.

Yakin neman zabe: APC ta soke zuwan Tinubu Kano

“Majalisar ta amince da cewa dole ne a cire tallafi na farko cikin gaggawa ba tare da wani ɓata lokaci ba, domin kuwa ba abu ne mai ɗorewa ba”. A cewar Zainab shamsuna

 

“Ba za mu iya ci gaba da biya ba. Dole mu kalli yadda cire tallafin ba zai jefa rayuwar ‘yan Najeriya ba cikin mawuyacin hali.

“Akwai buƙatar neman mafita bayan cire tallafin muna buƙatar yin shiri game da hakan domin tabbatar da an taimaka wa mutane da cire tallafin zai shafa.”

Gwamnatin Najeriya ta ce ta karɓo aron dalar Amurka miliyan 800 daga Bankin Duniya domin sassauta wa mutane raɗaɗin cire tallafin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...