Cutar kansar baki tana kashe yan Najeriya 764 a duk shekara – Gwamnatin Tarayya

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, ya ce cutar kansar baki da aka fi sani da kansar baka, na kashe mutane 764 a Najeriya duk shekara.

 

Ministan ya bayyana hakan ne jiya a Abuja yayin wani shirin horas da mutane yadda zasu kare kansu daga cutar kansar baka wanda gidauniyar Cleft and Facial Deformity Foundation (CFDF) ta shirya.

Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Shugabar sashin kula da hakora na ma’aikatar lafiya, Dr Gloria Uzoigwe, ce ta wakilci minjstan, ta ce Najeriya kuma na samun sabbin masu kamuwa da cutar daji guda 1,146 a duk shekara.

 

Ya ce ciwon daji na baki ya kasance daya daga cikin abubuwan da ke haifar da mace-mace mutane masu alaka da cutar daji a Najeriya saboda jinkirin rahoton da ake samu a asibitoci, da gazawar jami’an kiwon lafiya wajen gano cutar da wuri da kuma rashin isar da sako yadda ya kamata da dai sauransu.

 

Ministan ya ce gwamnati za ta kaddamar da wani sabon shirin kula da lafiyar baki a watan Nuwamba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...