Cutar kansar baki tana kashe yan Najeriya 764 a duk shekara – Gwamnatin Tarayya

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, ya ce cutar kansar baki da aka fi sani da kansar baka, na kashe mutane 764 a Najeriya duk shekara.

 

Ministan ya bayyana hakan ne jiya a Abuja yayin wani shirin horas da mutane yadda zasu kare kansu daga cutar kansar baka wanda gidauniyar Cleft and Facial Deformity Foundation (CFDF) ta shirya.

Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Shugabar sashin kula da hakora na ma’aikatar lafiya, Dr Gloria Uzoigwe, ce ta wakilci minjstan, ta ce Najeriya kuma na samun sabbin masu kamuwa da cutar daji guda 1,146 a duk shekara.

 

Ya ce ciwon daji na baki ya kasance daya daga cikin abubuwan da ke haifar da mace-mace mutane masu alaka da cutar daji a Najeriya saboda jinkirin rahoton da ake samu a asibitoci, da gazawar jami’an kiwon lafiya wajen gano cutar da wuri da kuma rashin isar da sako yadda ya kamata da dai sauransu.

 

Ministan ya ce gwamnati za ta kaddamar da wani sabon shirin kula da lafiyar baki a watan Nuwamba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...