Daga Aisha Aliyu Umar
Ma’aikatar kula da harkokin addinin Musulunci da wakafi ta kasar Kuwait ta bayyana haramta wa limamai karanta Alƙur’ani daga wayoyinsu na hannu a lokutan sallolin nafilfilun dare na watan Ramadana.
Jaridar Al-Rai ta ruwaito cewa hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ta samu sa hannun ƙaramin minista mai kula da harkar masallatai, Salah Al Shilahi.
Goman ƙarshe: Ya kamata matasa ku kashe Datar wayoyin ku, ku daina kallon TV – Dr. Ali Tamasi
Sanarwar ta ƙarfafa wa limamai gwiwa da su riƙa amfani da haddarsu ta Ƙur’ani a lokutan sallolin Tarawihi da Tahajjud, kasancewar su (limaman) misali ne ga sauran al’umma.
Ƙasar Ingila za ta dakatar da daukar ma’aikatan kiwon lafiya daga Najeriya
Ta ƙara da cewa ya kamata kowane limami ya yi muraji’ar karatunsa yadda ya kamata gabanin jan sallah a maimakon karantowa daga cikin waya.