Rasuwar Matar Aminu Dantata babban rashi ne ga jihar kano Inji Gwamna Ganduje

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano, ya mika ta’aziyyarsa ha hamshakin dan kasuwanan kuma guda cikin dattawan kano Alhaji Aminu Alhassan Dantata da daukacin iyalan Dantata bisa rasuwar uwargidansa Hajiya Rabi Aminu Alhassan Dantata.

 

Ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa ta gari waccce ta bada rayuwar ta wajen tarbiyantar da makusantanta bisa gaskiya da rikon amana.

 

“Hajiya Rabi Aminu Alhassan Dantata uwa ce mai kauna ga kowa, wadda adalcinta ya bata damar jagoranci ga wadanda ke kewaye da ita,” Ganduje ya yaba mata.

Mun kama yan sandan dake gadin mawaki Rarara – Rundunar yan sanda

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya aikowa kadaura24.

Hukumar jin dadin alhazai ta Kano ta sanar da dalilan da suka sa kudin hajjin bana ya yi tashin gwaron zabi

Gwamna Ganduje ya kara da cewa, “A madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga babban jigonmu, uba mai hangen nesa, Alhaji Aminu Alhassan Dantata bisa rasuwar marigayin. Hajiya Rabi Aminu Alhassan Dantata.”

 

Gwamna Ganduje ya bayyana rasuwar a matsayin “… babban rashi ne ba ga iyalanta kadai ba, har ma ga jihar da kuma sauran al’ummar salihai. Kamar yadda muke kaunar kasancewarta a tsakaninmu, Allah Ta’ala Ya fi kaunarta. Don haka. lokacinta a duniya ya wuce.”

 

“Allah Ya jikanta da Rahma, Ya kuma sa ta hutu ya yi mata sakamako da gidan Jannatul Fiddaus, Ya duba abin da ta bari”. A cewar Ganduje

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...