Ganduje ya kaddamar da kwamitin wayar da kan al’umma kan Kidaya

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawarin yin duk mai yiyuwa wajen ganin jihar ta cigaba da rike kambunta na jihar da tafi kowacce jihar yawan mutane, yayin aiki ƙidayar da za’a gudanar a bana.

 

Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan lokacin da yake kaddamar da yan kwamitin yada labarai wanda gwamnatin kano kafa domin wayar da akan al’umma muhimmancin kidayar.

Mun yi takaicin yadda muka rasa kujerar gwamnan kano – APC

Gwamna Ganduje wanda Sakataren gwamnati jihar Alhaji Usman Alhaji ya wakilta yace gwamnatin Kano ta ɗauki sha’anin kidayar da matukar muhimmanci, domin idan kana tafi kowacce jihar yawan mutane to zata Fi su amfana daga rabon tattalin arzikin kasa .

Sarkin Kano ya Jagoranci Sallar Jana’izar Matar Gwamnan Kano na farko

Yace an kafa kwamitoci da dama wadanda zasu taimaka wajen ganin an sami nasara kidayar ta bana, Kuma kwamitoci sun haɗa rukunonin al’umma daban-daban domin baiwa kowa damar bada tasa gudunmawar.

Yace za’a yi kidayar ne a makon farko na watan mayu wanda Kuma hakan ya nuna cewa lokacin gwamnatin Ganduje ce ke kan mulki , Amma duk da haka ta turawa Sabon zababben Gwamnan Kano da ya turo da wakilai wadanda za’a gudanar da aikin tare da su , saboda idan su ka zo mulki zasu samin cikakken bayanin abun da akai .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...