Ganduje ya kaddamar da kwamitin wayar da kan al’umma kan Kidaya

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawarin yin duk mai yiyuwa wajen ganin jihar ta cigaba da rike kambunta na jihar da tafi kowacce jihar yawan mutane, yayin aiki ƙidayar da za’a gudanar a bana.

 

Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan lokacin da yake kaddamar da yan kwamitin yada labarai wanda gwamnatin kano kafa domin wayar da akan al’umma muhimmancin kidayar.

Mun yi takaicin yadda muka rasa kujerar gwamnan kano – APC

Gwamna Ganduje wanda Sakataren gwamnati jihar Alhaji Usman Alhaji ya wakilta yace gwamnatin Kano ta ɗauki sha’anin kidayar da matukar muhimmanci, domin idan kana tafi kowacce jihar yawan mutane to zata Fi su amfana daga rabon tattalin arzikin kasa .

Sarkin Kano ya Jagoranci Sallar Jana’izar Matar Gwamnan Kano na farko

Yace an kafa kwamitoci da dama wadanda zasu taimaka wajen ganin an sami nasara kidayar ta bana, Kuma kwamitoci sun haɗa rukunonin al’umma daban-daban domin baiwa kowa damar bada tasa gudunmawar.

Yace za’a yi kidayar ne a makon farko na watan mayu wanda Kuma hakan ya nuna cewa lokacin gwamnatin Ganduje ce ke kan mulki , Amma duk da haka ta turawa Sabon zababben Gwamnan Kano da ya turo da wakilai wadanda za’a gudanar da aikin tare da su , saboda idan su ka zo mulki zasu samin cikakken bayanin abun da akai .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...