Sarkin Kano ya daga likkafar wasu hakimansa tare da nada sabbi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya daga Darajar wasu Hakimansa da kuma nada wasu sababbi.

 

Daga cikin Hakiman da aka daga Darajarsu sun hasar da Sarkin Dawakin Tsakar Gida Alhaji Ahmad Ado Bayero zuwa Dan Iyan Kano da Turakin Kano Alhaji Lamido Sunusi Bayero zuwa Sarkin Dawakin Tsakar Gida.

 

Tafidan Kano Alhaji Mahmoud Ado bayero ya zama Turakin Kano yayinda Dan Galadiman Kano Alhaji Haruna Rasheed Sunusi aka daga Darajarsa zuwa Tafidan Kano, sai Alhaji Kabiru Tijjani Hashim Dan Isan Kano ya zama Dan Galadiman Kano.

 

Ina godiya ga yan jaridu bisa hadin kan da suka ba ni – inji mai magana da yawun Ganduje Abba Anwar

Sauran sune Dan Lawan din Kano Alhaji Bashir Ado Bayero ya koma Dan Isan Kano, Alhaji Yahaya Inuwa Abbas Dan Majen Kano ya zama Lawan din Kano.

Abba Gida-gida ya shawarci  masu gine-gine a wararen Gwamnatin kano da su dakata

 

Kazalika Mai Martaba Sakin ya nada Alhaji Ahmad Kabiru Bayero a Matsayin Barde Kerarriya da kuma Alhaji Abdulkadir Mahmoud a Matsayin Magajin Rafin Kano.

 

A wata sanarwa da Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, yace jin kadan da nadasu, Mai Martaba Sakin yace an basu wadannan Sarautu ne saboda cancantaru da kuma hidimtawa al’umma.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukace su zamo jakadu nagari a duk inda suka sami kansu tareda ciyar da masarautar ta Kano gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...