Abba Gida-gida ya shawarci  masu gine-gine a wararen Gwamnatin kano da su dakata

Date:

Daga Abubakar Sa’id Sulaiman

Zababben Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf, na shawartar dukkanin masu yin gine-gine a filayen gwamnati da suka hadar da makarantu, kasuwanni, filayen wasanni da kuma badala da su dakata da wadannan aiyuka.

Emgr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan cikin ta cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran sa Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24 a daren jiya Alhamis.
  • ” Mun ɗauki wannan matakin ne saboda bukatar al’umma, Amma kuma duk wanda ya cigaba da yin gini a Inda aka hana to duk abun da ya faru ya kuka da kan shi”. A cewar Zaɓaɓɓen gwamnan kano
Idan ba a manta ba jam’iyyar NNPP da shi kan sa zaɓaɓɓen gwamnan ya Sha maganar cewa ba za su lamunci gine-gine a warare mallakin gwamnatin jihar kano ba , musamman idan suka zabo mulkin kano.
Sanarwar dai bata fayyace matakin da zaɓaɓɓen gwamnan zai ɗauka ba , akan Masu yin irin wadancan gine-gine, Amma mutane suna ta hasashen akwai yiwuwar a rushe gine-gine saboda anyi su ba bisa ƙa’ida ba.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ana zargin gwamnati Mai barin gado ba sayar da filayen ga yan kasuwa da sauran al’umma, wanda gwamnatin ta ce ta yi hakan ne domin kara bunkasa birnin kano da Kuma kasuwanci a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...