Gabanin zaben gwamnoni da na yan majalisu, yan Sanda sun tsaurara tsaro a Najeriya

Date:

Daga Maryam Ibrahim Zawaciki

An tsaurara tsaro a jahoji 28 cikin jahohi 36 na Najeriya inda za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jahohi a gobe Asabar.

Babban sifeton ‘yan sandan Najeriyar, Usman Baba, ya ayyana dokar hana zirga-zirgar ababen hawa a jahojin daga karshe 12 na tsakar daren Juma’a har zuwa karfe shida na yammacin ranar Asabar bayan kamala zaɓukan.

Ku yi amfani da damar ku wajen zabar shugabanni nagari don inganta rayuwar ku – Sarkin Kano ya fadawa al’ummar sa

Rahotanni sun ce an samu hatsaniya a tsakanin magoya bayan jam’iyyu a Jahar Legas, inda gwamnan Jahar mai ci na jam’iyyar APC, Babajide Sanwo-Olu, yake fuskantar zazzafar adawa daga ɗan takarar gwamnan Jahar na jam’iyyar Labour, Gbadebo Rhodes-Vivour.

Jam’iyyar ta Labour ce dai ta samu kuri’u mafi yawa a zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana watan jiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...