Ganduje ya yiwa Sarakunan Kano da Bichi ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsu

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana rasuwar Hajiya Maryam, Mai Babban Dakin Kano kuma matar marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero a matsayin babban Rashi ba ga al’ummar Jihar Kano ba kadai har da Kasa baki daya.

Ya nuna juyayinsa a madadin gwamnati da jama’ar jihar Kano ga Sarakunan Kano da Bichi, Alhaji Aminu Ado Bayero da Alhaji Nasiru Ado Bayero Daya bayan daya.

A cikin sakon ta’aziyya da kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar, gwamnan, wanda ya kara bayyana marigayiyar a matsayin uwa mai ladabi da gaskiya mai tarbiyantar da yayanta kan tafarkin Allah, ya yi wa sarakuna ta’aziyyar Rasuwar mahaifiyarsu.

Ganduje ya ce mutuwar ta a wannan lokacin ta haifar da wani yanayi mai wahalar cikewa musamman ga ‘ya’yan ta maza guda biyu wadanda ke matukar bukatar jagora da shawarwari daga uwa.

Gwamnan ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya sanya marigayir a Aljannah Firdausi da kuma karfin gwiwa ga dangin, da daukacin mutanen da ke Masarautar guda biyu don jure wannan babban rashi.

80 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilan da suka sa Kwankwaso ba zai hada hanya da Tinubu a zaben 2027 ba – Buba Galadima

Guda cikin jiga-jigan jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce...

Adam A Zango ya sake Aurar Jarumar Kannywood

Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finan Hausa, Kannywood, Adam A....

NNPP ta yi watsi da sakamakon Zaben Ghari da Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta ƙi amincewa da...

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...