Ku Karbi Kaddara Idan Kuka Fadi Zabe – Buhari ya fadawa yan takarar shugaban kasa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Shugaba Muhammadu Buhari ya buƙaci dukkan ‘yan takarar kujeru daban-daban a babban zaɓen ƙasar da ke tafe a ranar Asabar da su mutunta ‘yancin masu zaɓe da kuma karɓar sakamakon zaɓen da hannu biyu.

Buhari na magana ne a Abuja jiya Laraba, yayin wani taro da Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa ya shirya domin ganin jam’iyyu da ‘yan takarar kujerar shugaban ƙasa sun sa hannu na yarjejeniyar yin zaɓe lafiya.

Talla

Shugaban Najeriyar ya kuma buƙaci wadanda suka ki karɓar sakamakon zaɓen da su bi kadinsu ta hanyar shari’a.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

“Ina kira ga dukkan ‘yan takara na kujeru daban-daban a wannan zaɓe da su tabbata sun mutunta ‘yancin masu zaɓe da kuma karɓar sakamakon zaɓe da hukumar zaɓe za ta sanar, wanda sune dka ta bai wa damar yin hakan,” in ji Buhari.

Shugaban ya kuma yaba wa kwamitin zaman lafiya na ƙasa, inda ya ce duk da cewa babu wani taimako na kuɗi da gwamnati ke bai wa kwamitin, ta dai ci gaba da aiki da hukumomi daban-daban domin ganin abubuwa sun tafi daidai da kuma ƙoƙari wajen shiga tsakani kan sha’anin zaɓe.

Shugaba Buhari ya ce yana sane da damuwa da ake nunawa kan yadda za a gudanar da zaɓen da kuma yadda abubuwa za su kasance bayan bayyana sakamakon zaɓen.

Ya ce tun zuwa kan mulki, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen tabbatar da ta bar abin tarihi na gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...