Tarukan Siyasa: Rundunar Yan Sanda Kano ta baiwa jam’iyyun APC NNPP da PDP Shawara

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta gana da wakilan jam’iyyun APC NNPP da PDP domin a shawo kansu game da yakin neman zabe da jam’iyyun suka shirya gudanarwa yau Alhamis a Kano.
Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan yan sanda na jihar kano CP Muhammad Yakubu ne ya jagoranci Zaman wanda aka yi shi da zummar sanar da su illar da yin tarukan nasu a rana guda zai haifar da Kuma yiyuwar samun matsala ga Zaman lafiya da ake da shi a Kano.
Talla
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a safiyar yau Alhamis.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
” Bayan samun labarin dukkanin wannan jam’iyyu guda uku suna son gudanar da tarukan yaƙin neman zabe a yau Alhamis, hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Muhammad Yakubu ya gayyato wakilan jam’iyyun donin samun masalaha , Amma daga karshe dai masalahar bata Samu ba”. Inji
Kiyawa ya ce kwamishinan ya baiwa jam’iyyun shawarar dukkanin su su hakuri da yin taron, su bari sai bayan zaben Shugaban Kasa wanda za’a yi ranar Asabar Mai zuwa saboda kusancin da wuraren taron ke da shi ga na wata jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...