Bayan tuban Murja Kunya Mai Shari’a ya sake Mai da ita Gidan Yari ita da wasu yan TikTok

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A yau Alhamis, 16 ga watan Febrairu, shahrarriyar yar dandalin TikTok, Murja Ibrahim Kunya, ta sake gurfana gaban kotun shari’ar Musulunci dake Filin Hoki jihar Kano.

 

An kuma tisa keyyar Aminu Ibrahim da Sadiq Sharif Umar, da Ashiru Idris mai wushirya bisa zargin kalaman batsa a shafin Tiktok zuwa gidan yari mako 1.

 

 

Talla
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Laifukan da ake tuhumar su ka iya bata tarbiyar yara masu tasowa, wanda su ka kuma saba da sashi na 355 da 356 da kuma 358 na kundin laifuffuka na kotun Shari’ar Musulunci.

 

Murja Ibrahim kunya ta musanta tuhumar da ake yi mata amma abokin burmunta Ashiru Idris mai wushirya ya amsa laifin sa.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa kotun ta aike da Murja Ibrahim Kunya gidan yari sakamakon wata kara da wasu Malamai a kano suka shigar kan rashin tarbiyya da Murja ta ke yi a shafukan sada zumunta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...