Bayan tuban Murja Kunya Mai Shari’a ya sake Mai da ita Gidan Yari ita da wasu yan TikTok

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A yau Alhamis, 16 ga watan Febrairu, shahrarriyar yar dandalin TikTok, Murja Ibrahim Kunya, ta sake gurfana gaban kotun shari’ar Musulunci dake Filin Hoki jihar Kano.

 

An kuma tisa keyyar Aminu Ibrahim da Sadiq Sharif Umar, da Ashiru Idris mai wushirya bisa zargin kalaman batsa a shafin Tiktok zuwa gidan yari mako 1.

 

 

Talla
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Laifukan da ake tuhumar su ka iya bata tarbiyar yara masu tasowa, wanda su ka kuma saba da sashi na 355 da 356 da kuma 358 na kundin laifuffuka na kotun Shari’ar Musulunci.

 

Murja Ibrahim kunya ta musanta tuhumar da ake yi mata amma abokin burmunta Ashiru Idris mai wushirya ya amsa laifin sa.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa kotun ta aike da Murja Ibrahim Kunya gidan yari sakamakon wata kara da wasu Malamai a kano suka shigar kan rashin tarbiyya da Murja ta ke yi a shafukan sada zumunta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...