Gwamna Matawalle Ya Bada Umarnin Kama Masu Kin Karɓar Tsofaffin Kuɗade A Zamfara

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya bada umarnin kama duk wanda ya ki karban tsofaffin kudi na naira dari biyu, dari biyar da dubu daya a jihar.
 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jamilu Iliyasu Birnin Magaji, sakataren yada labaran gwamnan jihar ya fitar a ranar Juma’a.
 Sanarwar ta ce Matawalle ya bayyana hakan ne a wajen bikin rantsar da sabbin alkalan babbar kotuna da sabbin masu ba da shawara na musamman da aka nada a gidan gwamnati, dake Gusau, babban birnin jihar.
Talla
 A cewar sanarwar, shi da takwarorinsa na jihohin Kogi da Kaduna suna neman kotun kolin kasar da ta ba da umarnin tsawaitawa tare da cigaba da amfani tsoffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1000.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Gwamna Bello Matawalle ya kuma yabawa kotun koli bisa yin abin da ya kamata, wanda a cewarsa hakan zai rage radadin halin da talakawa su ke ciki.
 Ya bayyana farin cikinsa cewa yanzu tsohon kudin ya fara aiki kuma har yanzu mutane na iya amfani dasu a harkokin su na kasuwanci .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...