Chanjin kudi: Akwai bukatar mawadata su tallafawa mabukata – Munzali Sani Musa

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Wani dan kasuwa a nan kano Alh munzali Sani Musa ya bukaci mawadata dake cikin al’umma dasu tallafawa mabukata gwargwadon iko duba da halin matsi da al’umma  ke ciki musamman da abinda zasu cigaba da gudanarda da rayuwarsu.

 

Kadaura24 ta rawaito Alhaji munzali sani Musa ya bayyana hakanne a yayin da yake ganawa  da manema labarai a ofishinsa.

 

Ya ce yawan sadaka da kyauta baya rage yawan dukiya, sai dai ya kara habbaka ta  kamar yadda Allah subhanahu wata Allah ya bayyana a cikin Alkurani mai girma, cewa duk abinda ka bayar zai dawo maka dashi.

Talla

“Ku  taimakawa al’umma da abun da Allah ya hore muku domin rage musu radadin halin da suke ciki , idan kukayi hakan Allah zaiyi farin ciki da hakan” . Inji Alh. Munzali Sani

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Ya kuma Kara da cewar Annabi sallallah Alaihi wasallam yace kayi sadaka koda da barin dabino ne, ka baiwa dan uwanka shi ma. Allah yana farin ciki da hakan.

 

Yace mutukar mawadata dake jihar nan suka jajirce wajan tallafawa yan uwansu da sauran al’umma dake tare dasu, babu shakka za a sami sauki a halin Kunchi da ake ciki musamman ta hanyar samar musu abincin da sauran bukatun sa na yau da kullum.

Ya bayyana cewa duk wanda Allah ya yalwata masa da dukiya babban abinda zai yi wajan ganin dukiyar nan ta dawwama shi ne tallafawa mubakata ta fannoni da dama, Hakika Allah zai sanya Albarka a wannan dukiya dama zuriarsa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...