Jam’iyyar adawa ta NDC ta ce za ta nemi gudunmawar kudi daga talakawan Najeriya domin gudanar da yakin neman zabenta a zaben 2027.
Uban jam’iyyar na kasa, Sanata Seriake Dickson ne ya bayyana haka yayin wata hira da gidan talabijin na Arise News a ranar Laraba.

Sanata Dickson, wanda ke wakiltar Bayelsa ta Yamma a Majalisar Dattawa, ya ce NDC ce jam’iyyar siyasa daya tilo a Najeriya da ba ta samun kudin gudanar da ayyukanta daga baitul malin gwamnati.
Ya ce jam’iyyar na shirin bai wa yan Najeriya damar bayar da gudunmawa daga Naira 1,000 zuwa Naira 2,000 domin taimakawa wajen gudanar da ayyukanta da yakin neman zabenta.
“Ba za a bar dimokuradiyyarmu ta dogara da kudin attajirai da biliyoyin kudi na gwamnati ba,” in ji Sanata Dickson.

Ya kuma ce jam’iyyar na tuntubar masu ruwa da tsaki kan wadanda za su kasance cikin kwamitin yakin neman zabenta na shugaban kasa, yana mai cewa za a sanar da sunayensu nan ba da jimawa ba.