Suyudi Isah Jibril Bichi ya zama sabon Manajan gidan Rediyon Tech FM dake Kano

Date:

Hukumar gudanarwar gidan Rediyon Tech FM dake jihar Kano ta amince da nada Suyudi Isah Jibril Bichi a matsayin sabon Manajan tashar.

Wannan na kunshe ne cikin wata takardar da aka fitar ranar 13 ga Oktoba, 2025, wacce Manajan Darakta na kamfanin, Mukhtar Tajuddeen Usman, ya sanya wa hannu kuma aka aikowa Kadaura24, inda aka bayyana cewa nadin zai fara aiki nan take.

Suyudi Isah Jibril Bichi yana da Dibloma da digiri na farko (BSc) a fannin aikin Jarida, sannan a halin yanzu yana ci gaba da karatun digiri na biyu (Masters) a fannin hulda da jama’a (Public Relations) a Jami’ar Bayero Kano (BUK).

Suyudi Bichi na da ƙwarewa mai zurfi a harkar yada labarai da aikin jarida, wanda ya samu gogewa ta tsawon shekaru sakamakon aiki da ya yi a kafafen watsa labarai daban-daban.

Kafin wannan mukami, Suyudi Bichi ya rike matsayin Manaja a Guarantee Radio, inda ya shafe shekaru biyu yana gudanar da wannan aiki cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...