Suyudi Isah Jibril Bichi ya zama sabon Manajan gidan Rediyon Tech FM dake Kano

Date:

Hukumar gudanarwar gidan Rediyon Tech FM dake jihar Kano ta amince da nada Suyudi Isah Jibril Bichi a matsayin sabon Manajan tashar.

Wannan na kunshe ne cikin wata takardar da aka fitar ranar 13 ga Oktoba, 2025, wacce Manajan Darakta na kamfanin, Mukhtar Tajuddeen Usman, ya sanya wa hannu kuma aka aikowa Kadaura24, inda aka bayyana cewa nadin zai fara aiki nan take.

Suyudi Isah Jibril Bichi yana da Dibloma da digiri na farko (BSc) a fannin aikin Jarida, sannan a halin yanzu yana ci gaba da karatun digiri na biyu (Masters) a fannin hulda da jama’a (Public Relations) a Jami’ar Bayero Kano (BUK).

Suyudi Bichi na da ƙwarewa mai zurfi a harkar yada labarai da aikin jarida, wanda ya samu gogewa ta tsawon shekaru sakamakon aiki da ya yi a kafafen watsa labarai daban-daban.

Kafin wannan mukami, Suyudi Bichi ya rike matsayin Manaja a Guarantee Radio, inda ya shafe shekaru biyu yana gudanar da wannan aiki cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...