Tinubu ya bukaci Majalisa ta amince ya ciyo bashin dala biliyan $2.35

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rubuta wa majalisar wakilai yana neman amincewarta domin ciyo bashin dala biliyan $2.347 daga kasuwar kuɗin ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025 da kuma sake biyan tsohon bashin Eurobond da zai ƙare a watan Nuwamba 2025.

Haka kuma, Shugaban ƙasar yana neman amincewar majalisar wajen fitar da tsarin bashi mara Ruwa na Sukuk na farko a duniya, wanda darajarsa ta kai dala miliyan $500, domin aiwatar da manyan ayyukan more rayuwa.

Tinubu ya ce buƙatar tana da tushe bisa ga tanade-tanaden Dokar Hukumar Gudanar da Bashi ta Ƙasa ta 2003, tare da nufin ƙarfafa damar Najeriya wajen samun kuɗaɗen kasashen waje da kuma gujewa jinkirin biyan bashi.

Ya bayyana cewa gwamnati za ta yi amfani da hanyoyi daban-daban wajen ɗaukar bashin, ciki har da Eurobond, bashin haɗin gwiwa, ko lamunin kai tsaye daga cibiyoyin kuɗi na duniya.

A cewar Tinubu, tsarin Sukuk ɗin da ake shirin fitarwa zai taimaka wajen gina ababen more rayuwa da kuma haɓaka kasuwar takardun gwamnati kamar yadda aka yi da Sukuk na cikin gida tun daga shekarar 2017.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...