Da dumi-dumi: Ministan Tinubu ya yi Murabus

Date:

Ministan Kimiyya da Fasaha na Najeriya, Uche Nnaji, ya yi murabus daga mukaminsa.

Hakan ma kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun fadar shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya tabbatar.

 

Rahotanni sun bayyana cewa ministan ya tsinci kansa cikin ce-ce-ku-ce ne tun bayan wani binciken jaridar Premium Times da ya gano cewa takardar shaidar karatun sa (degree) da takardarsa ta bautar Kasa NYSC na jabu ne.

Shugaban jami’ar Nsukka (UNN), Farfesa Simon U. Ortuanya, ya bayyana wa Premium Times cewa duk da cewa Nnaji ya fara karatu a jami’ar a shekarar 1981, bai kammala karatunsa ba, kuma jami’ar bata taɓa ba shi shaidar kammala digiri ba.

Sai dai sanarwar da Bayo Onanuga ya fitar ta ce Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya karbi murabus din nasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...