Da dumi-dumi: Tinubu zai yi wa yan Nigeria jawabi

Date:

 

 

Shugaban kasa Bola Tinubu zai yi jawabi ga kasa da misalin karfe 7 na safe ranar Alhamis a matsayin wani bangare na bukukuwan ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Tinubu zai kuma halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya.

Kwamitin bikin ranar dimokuraɗiyya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Abdulhakeem Adeoye, wanda ya fitar da sanarwar a madadin Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na kwamitin, ya ce bayan jawabin da shugaban kasa zai yi, zai halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya da misalin karfe 12 na rana.

Zan yi amfani da shirin GEEP don inganta rayuwar matasa Nigeria – Hamza Ibrahim Baba

Sai dai, a cewar Adeoye, ba za a gudanar da bikin faretin Ranar Dimokuraɗiyya ba. Daga bisani a ranar, za a gudanar da muhawara ta musamman dangane da bikin ranar Dimokuraɗiyya a Dakin Taro na Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja da misalin karfe 4 na yamma.

InShot 20250309 102403344

Taken wannan muhawara shi ne: “Ƙarfafa Nasarorin Dimokuraɗiyyar Najeriya: Bukatar Sauye-sauye masu Dorewa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Al’ummar Garin Rimin Zakara Sun Sake Fadawa Halin Rashin Tabbas

Daga Rayyan Hassan   Al'ummar garin Rimin Zakara dake karamar hukumar...

Zargin cin Bashi: Gwamna Abba bai taba ciyo bashi ba – Gwamnatin Kano

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta musanta zargin...

Gwamnatin Kano ta taya Makwarari murnar zama shugaban tashar Himma Radio

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta taya sabon...

Gwamna Abba ya jinjinawa hukumomin ba da agajin gaggauwa, bisa dakile iftila’i tankar Mai a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabair...