Da dumi-dumi: Tinubu zai yi wa yan Nigeria jawabi

Date:

 

 

Shugaban kasa Bola Tinubu zai yi jawabi ga kasa da misalin karfe 7 na safe ranar Alhamis a matsayin wani bangare na bukukuwan ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Tinubu zai kuma halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya.

Kwamitin bikin ranar dimokuraɗiyya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Abdulhakeem Adeoye, wanda ya fitar da sanarwar a madadin Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na kwamitin, ya ce bayan jawabin da shugaban kasa zai yi, zai halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya da misalin karfe 12 na rana.

Zan yi amfani da shirin GEEP don inganta rayuwar matasa Nigeria – Hamza Ibrahim Baba

Sai dai, a cewar Adeoye, ba za a gudanar da bikin faretin Ranar Dimokuraɗiyya ba. Daga bisani a ranar, za a gudanar da muhawara ta musamman dangane da bikin ranar Dimokuraɗiyya a Dakin Taro na Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja da misalin karfe 4 na yamma.

InShot 20250309 102403344

Taken wannan muhawara shi ne: “Ƙarfafa Nasarorin Dimokuraɗiyyar Najeriya: Bukatar Sauye-sauye masu Dorewa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...