Daga Usman Hamza
Shugaban majalisar limaman masallatan juma’a na Nigeria sheikh Muhammad Nasir Adam ya bukaci Al’ummar kasar nan da su dage wajan nema gafara da kuma yawaita aiki nagari a cikin kwanaki goma na farkon watan Zulhija da mu ke ciki.
Sheikh Nasir Adam ya yi wannan jawabin a kasa mai tsarki ta cikin wani sako da ya aikowa Kadaura24.

Sheikh Nasir ya ce Wadanan kwanaki ne da bawa zai kara zage dantse wajan ibada, kamar yin sallar farillah cikin Jam’i, biyemasu da nafil-file, zakiri da salatin Annabi S A W harama da yin ibadar Azumi inda Allah yaba mutun iko.
kazalika Sheikh Muhammad Nasir Adam yace duk Wani mumini a irin wannan lokaci yana kokarin aikin da Allah zai kara yadda da shine domin kara kusanci ga mahalicci.
Da yake bayani ga maniyatan Nigeria wadanda su ka amsa kiran Allah ya bayyana cewa lailai ne su matsa da addu’a ga kawunansu da kuma kasa Nigeria da jihohinsu domin samun zaman lafiya da yalwar arziki.
Daga karshe shugaban majalisar limamin masallatan juma’a na Tarayyar Nigeria sheikh Muhammad Nasir Adam yayi addu’a ga Malamai ,’Yan Kasuwa, Ma’aikata, dalibai, matasa, Shugabani da sauran Al’ummar Gari akan neman taimakon Allah a cikin lamarinsu.