Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware kudi domin sake gina masallacin da wani mutum ya bankawa wasu masallata wuta yayin da suke sallar asuba a karamar hukumar Gezawa.

A wata sanarwa da jami’in yada labaran yankin Jamilu Mustapha Yakasai ya aikowa Kadaura24, ya ce Shugaban karamar hukumar Gezawa, Alhaji Mukaddas Bala Jogana, ya bayyana cewa, baya ga sake gina masallacin, gwamnatin za ta kuma gina ajujuwa, da bandakuna, da rijiyar burtsatde a harabar masallacin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Mukaddas ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kammala aikin titin kilomita 5 na karamar hukumar.

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Ya yi kira ga ma’aikatar ayyuka da ta fara aikin titin Dan Madanho zuwa Kwasangwami zuwa Zango, wadda ya ce hanya ce mai muhimmanci da al’umma da dama ke amfani da ita.

Alhaji Mukaddas Bala ya nuna matukar godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kokarinsa na daukaka martabar jihar Kano. Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su ci gaba da marawa gwamnatin gwamna Abba Kabir Yusuf baya.

InShot 20250309 102403344

Shugaban karamar hukumar Gezawan ya yi alkawarin za’a ci gaba da gudanar da ayyukan raya kasa don amfanin al’ummar yankin, musamman a fannonin kiwon lafiya, ilimi, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...