Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

Date:

 

Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al’umma, kuma ɗan jam’iyyar APC, Ambasada Mustapha Salisu Akarami, ya ƙaddamar da gangamin duba lafiyar al’ummar mazaɓar Garko da Raɓa, da ke ƙaramar hukumar Garko, a Kano, su 1400, tare da basu magungunan miliyoyin Kuɗi kyauta.

 

Ambasada Mustapha Salisu Akarami, ya ce ya ɗauki nauyin ƙwararrun Likitoci, don duba lafiyar mutanen tare da basu magungunan kyauta, domin rage musu wata damuwa bisa halin matsin rayuwa da ake ciki.

InShot 20250309 102403344

An duba lafiyar mutanen ne ranar Asabar, a babban Asibitin ƙaramar hukumar Garko, wanda al’umma suka yi fitar ɗango, aka duba lafiyar su a ɓangaren cututtuka daban-daban, tare da basu magungunan kyauta, da kuma basu shawarwarin yadda za su kula da lafiyar su.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ambasada Mustapha Salisu Akarami, ya kuma ce yanzu haka yana shirye-shiryen yin zagaye na biyu na gangamin duba lafiyar al’ummar sauran mazaɓun ƙaramar hukumar ta Garko tare da fito da wasu tsare-tsare da za su taimaki mutanen yankin.

Ga hotunan yadda taron duba marasa lafiyar ya gudana

IMG 20250518 WA0012 IMG 20250518 WA0013 IMG 20250518 WA0010

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...

Bayan ajiye aiki, Sojojin Nigeria 24 sun tsunduma tafiyar kwankwasiyya

Tsaffin sojojin Najeriya da suka ajiye aiki su 24...