2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Date:

Daga Zakariya Adam Jigirya

 

Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa ya musanta cewa yana nema kujerar gwamnan jihar Kano ko Sanatan kano ta kudu a zaben 2027.

“Na jima ina bayyanawa karara cewa ba ni da sha’awar tsayawa takarar Sanatan Kano ta Kudu, ko kuma kujerar gwamnan jihar Kano a 2027. Duk da haka, ban yi mamakin yadda ako da yaushe sunana yake zama a sahun gaba akan duk wasu batutuwa irin wannan ba”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kadaura24 ta rawaito Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana hakan ne cikin wani sako da ya wallafa a sahihin shafinsa na Facebook .

Ya ce a koda yaushe yana godewa Allah saboda ni’imar da yayi masa a siyasa, ya ce ya ci zaben dan majalisar wakilai karo gudu a jam’iyyu daban-daban, sannan ya rike mukamai daban-daban a matakin majalisa da gwamnatin tarayya.

A Gaggauce: Gwamnan Kano ya dakatar da hadiminsa

“Wadanda suka san ni da kyau sun san cewa duk inda na tsinci kaina a siyasance ko ma a harkokin kasuwanci na kafin na shiga tsiyasa da harkokin koyarwa a jami’a Ina jajircewa don ganin na sami nasara”.

InShot 20250309 102403344

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito an jima ana hasashen Abdulmumin Jibrin Kofa zai nemi takarar gwamnan Kano ko Sanatan kano ta kudu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...