Bayan ajiye aiki, Sojojin Nigeria 24 sun tsunduma tafiyar kwankwasiyya

Date:

Tsaffin sojojin Najeriya da suka ajiye aiki su 24 sun mika wuya ga tafiyar kwankwasiyya karkashin jagorancin Madugunta Sanata Rabiu Musa kwankwaso.

Tsaffin sojojin sunce sun rungumi tsarin Kwankwasiyya ne domin bada tasu gudu mowar a zaben 2027 musamman burinsu na ganin Kwankwaso yayi nasara a siyasarsa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Tsaffin sojojin da suka ajiye aiki a watan Janairu na 2025 bayan wa’adin Shekara 35 suna aiki sun bayyana cikakken goyon bayansu ga akidar Kwankwasiyya.

A Gaggauce: Gwamnan Kano ya dakatar da hadiminsa

A wata ziyara da suka kaiwa sanata Rabiu Musa kwankwaso a gidansa karkashin jagorancin Shugaban hukumar bada tallafin Karatu ta jihar Kano,Dr Kabiru Getso Haruna,ya bayyana ziyarar ta tsaffin sojojin a matsayin wata babbar nasara ga tafiyar kwankwasiyya a Najeriya.

A jawabinsa, Madugun kwankwansiyyar Sanata Rabiu Musa kwankwaso ya yabawa sojojin a bisa sadaukarwa da sukayi lokacin da suke aiki.

InShot 20250309 102403344

“Gashi kun dauki lokaci mai tsawo kun sadaukar Lokacin aiki soja, yanzu kuma kuna so ku sake sadaukarwa a tafiyar Demokaradiya,a dan haka dole a yaba muku”,Inji Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...