Shugaban Karamar hukumar Wudil ya tallafawa wasu amare da kayan daki

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugaban Karamar hukumar Wudil Abba Muhammad Tukur ya yi alkawarin tallafawa iyaye domin su sami sukunin aurar da ‘yayansu musamman mata.

“Mun san halin da al’umma suke ciki shi yasa muka dabbaka irin wannan tsarin wanda jagoranmu Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya fara yi a Kano, na tallafawa iyaye domin su sami damar aurar da ‘yayansu”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Abba Muhammad Tukur ya bayyana hakan ne lokacin da yake mika kayan daki ga iyayen wasu amare guda biyu da suke yan asalin karamar hukumar Wudil.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Shugaban Karamar hukumar Wudil kan harkokin yada labarai Abba Ashiru ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Za mu yi aikin hanyar Utai zuwa Kademi – Shugaban karamar hukumar Wudil

Ya ce zai cigaba da duk mai yiwuwa don tallafawa iyayen yara a yankin musamman iyayen yaran da ba su da karfi.

A jawabinsu daban-daban iyayen Amaren sun godewa shugaban karamar hukumar ta Wudil bisa tausayi da imani da ya nuna wajen dauke musu nauyi kayan dakin da ya rataya a wuyansu.

InShot 20250309 102403344

Wadanda aka baiwa kayan dankin dai daya ta fito ne daga mazar cikin garin wudil yayin da guda kuma ta fito daga mazabar utai duk a karamar hukumar Wudil.

Kayan dakin da shugaban karamar hukumar Wudil Abba Muhammad Tukur ya tallafawa amaren da su sun hadar da Gado da katifa, sai kujeru da madubi da fulollata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...