NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar Kula da aikin hajji ta Najeriya ta ce ta kwashe maniyyatan Najeriya 24,744 zuwa kasar Saudiyya don gudanar da aikin hajjin shekarar 2025 a cikin kwanaki 10.

NAHCON ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da babban jami’in yada labaranta, Malam Shafil Mohammed, ya fitar a Abuja.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima ne a ranar 9 ga watan Mayu, ya kaddamar da fara tashin Maniyatan na jirgin na farko a Owerri, Imo.

Mohammed, ya ce a cikin kwanaki goma, jirage 61 sun yi nasarar jigilar alhazan Najeriya 24,744 zuwa kasar Saudiyya.

A Gaggauce: Gwamnan Kano ya dakatar da hadiminsa

Ya ce hukumar za ta rika sanar da jama’a irin ci gaban da aka samu kan aikin.

InShot 20250309 102403344

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, NAHCON wata hukuma ce ta gwamnati da ke tsarawa tare da kula da ayyukan Hajji da Umrah ga Musulman Najeriya don tabbatar da tafiyar hajji cikin sauki da inganci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...