Buhari ne ya cire tallafin man fetur ba Tinubu ba – Sanata Kawu Sumaila

Date:

Daga Ummahani Abdullahi Adakawa

 

Dan majalisar dattawa mai wakiltar Kano ta Kudu, Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila, ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya cire tallafin man fetur ba shugaba Bola Tinubu ba.

Kawu Sumaila ya bayyana hakan ne a a wata hira da aka yi da shi yau laraba a shirin Politics Today na gidan Talabijin na Channels TV.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya bayyana cewa dama a kasafin kudin shekara ta 2023, da Buhari ya yi ya tanadin kudin tallafin man fetur na zangon farko na shekarar ne kawai.

Gwamnatin Kano ta magantu kan batun sayawa sarki Sanusi motocin Miliyan 670

Ya ce Tinubu ya sanar da cire tallafin ne bayan gwamnatin da ta shude ta rika ta cire.

InShot 20250309 102403344

“Gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ce ta cire tallafin man fetur saboda dama ba ya cikin kasafin kudin shekara, a wannan shekarar an sanya tallafin man fetur ne daga watan Janairu zuwa Yuni, daga ranar ba za a saka ba da tallafin man fetur ba, kawai sanar da cire tallafin man fetur Tinubu amma ba shi ya cire ba”. Inji Kawu Sumaila

Sanata Kawu Sumaila dai bai jima da shiga jam’iyyar APC ba, bayan da ya fice daga jam’iyyar NNPP ta Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...